Kasar rasha ta gargadi kasashen yammacin Africa
Ƙasar Rasha ta gargaɗi ƙungiyar Ecowas game da ɗaukar matakin soji da ta ce za ta yi kan sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar.
Tana mai cewa matakin ka iya haifar da rikicin da zai daɗe ba a ga ƙarshensa ba.
Cikin wata sanarwa da ma'aikatar harkokin wajen Rasha ta fitar ranar Juma'a ta gargaɗi ƙasashen yammacin Afirka da kada su aika sojoji zuwa Nijar.
Sanarwar ta ce ''Mun yi imanin cewa matakin soji ba zai warware matsalar Nijar ba, a maimakon haka lamarin zai haifar da mummunan rikici, wanda ba a san ranar ƙarewarsa ba, tare da sake dagula lamura a yankin Sahel''.
Manyan hafsoshin tsaron ƙasashen Ecowas na shirin wata ganawa a ranar Asabar domin tsara yadda za a shirya dakarun sojin.

Comments
Post a Comment